Jummaʼa 8 Mayu 2026 - 23:22
Silsilar Tattaunawa Kan Mahdawiyya (25) | Raja'a a cikin Alƙur'ani da Hadisai

Hauza/ Bisa ga ayoyin Alƙur’ani da ruwayoyin Ahlul Bayt (A.S.), wani rukuni daga cikin matattu zasu dawo da rai a duniya a zamanin bayyanar Imam Mahdi (A.S.).

Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito, jerin darussan Mah­dawiyya mai taken “Zuwa ga al’umma Mai Manufa”, ana gabatar da shi ne domin yada koyarwa da ma’arifa da suka shafi Imam az‑Zaman (A.J.).

A cikin ayoyi daban‑daban na Alƙur’ani Mai Girma, an ambaci dawowar wasu daga cikin matattu zuwa duniya.

Annabi Uzair (A.S.)

Annabi Uzair (A.S.), bayan ya mutu shekaru ɗari (100), Allah Ya tashe shi, ya kuma dawo duniya ya yi rayuwa ta dogon lokaci.

«أَوْ کَالَّذِی مَرَّ عَلَیٰ قَرْیَةٍ وَهِیَ خَاوِیَةٌ عَلَیٰ عُرُوشِهَا قَالَ أَنَّیٰ یُحْیِی هَٰذِهِ اللَّهُ بَعْدَ مَوْتِهَا فَأَمَاتَهُ اللَّهُ مِائَةَ عَامٍ ثُمَّ بَعَثَهُ قَالَ کَمْ لَبِثْتَ قَالَ لَبِثْتُ یَوْمًا أَوْ بَعْضَ یَوْمٍ قَالَ بَلْ لَبِثْتَ مِائَةَ عَامٍ فَانْظُرْ إِلَیٰ طَعَامِکَ وَشَرَابِکَ لَمْ یَتَسَنَّهْ وَانْظُرْ إِلَیٰ حِمَارِکَ وَلِنَجْعَلَکَ آیَةً لِلنَّاسِ وَانْظُرْ إِلَی الْعِظَامِ کَیْفَ نُنْشِزُهَا ثُمَّ نَکْسُوهَا لَحْمًا ۚ فَلَمَّا تَبَیَّنَ لَهُ قَالَ أَعْلَمُ أَنَّ اللَّهَ عَلَیٰ کُلِّ شَیْءٍ قَدِیرٌ.» 

"Ko kuma kamar wanda ya wuce kusa da gari da ya rushe gaba ɗaya, sai ya ce: "Yaya Allah zai farfaɗo da waɗannan bayan mutuwarsu?" Sai Allah Ya kashe shi shekaru ɗari sannan Ya tashe shi. Ya tambaye shi: "Kwana nawa ka yi"? Ya ce: "Kwana guda ko wani ɓangaren rana. Allah Ya ce: "A’a, shekaru ɗari ka yi. Dubi abincinka da abin shanka, ba su lalace ba. Ka kuma dubi jakinka…" Lokacin da lamarin ya bayyana gare shi, sai ya ce: Na sani lallai Allah Mai iko ne a kan komai.

Fitattun (Zaɓaɓɓun) mutanen Bani Isra’ila

Mutane saba’in daga cikin manyan mutanen Annabi Musa (A.S.) sun tafi tare da shi zuwa dutsen Ɗur domin su kasance shaidu a lokacin da Annabi Musa (A.S.) zai karɓi Alluna (Al'wah) daga Allah. Amma bayan sun ga al’amuran Musa, sai suka ce: "Ba za mu yi imani ba sai mun ga Allah a fili." Musa (A.S.) ya hana su, amma suka nace. Sai tsawa ta buge su suka mutu. Musa ya damu, ya roƙi Allah Ya dawo da su, Allah kuma Ya tashe su.

“ثُمَّ بَعَثْنَاكُمْ مِنْ بَعْدِ مَوْتِكُمْ لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ.”

"Sannan muka tashe ku domin ku yi godiya." (Suratul Baƙarah, 56)

Raj’a zuwa duniya a nan gaba

«وَیَوْمَ نَحْشُرُ مِنْ کُلِّ أُمَّةٍ فَوْجًا مِمَّنْ یُکَذِّبُ بِآیَاتِنَا فَهُمْ یُوزَعُونَ.» 

A wata rana, za mu tara rukuni daga kowace al'umma waɗanda suka ƙaryata ayoyinMu; za a riƙe su su jirar juna." (Suratul Naml, 86)

Wannan ba ranar kiyama ba ce, domin a kiyama duk mutane za a tashe su:

«وَیَوْمَ نُسَیِّرُ الْجِبَالَ وَتَرَی الْأَرْضَ بَارِزَةً وَحَشَرْنَاهُمْ فَلَمْ نُغَادِرْ مِنْهُمْ أَحَدًا.» 

"Kuma a ranar da Za Mu tafiyar da duwatsu, kuma za ka ga ƙasa a bayyane, sannan Mu tattara su, ba za Mu bar ko ɗaya daga cikinsu ba."

Tabarsi ya rubuta a Majma‘ al‑Bayan cewa bisa ruwayoyi masu yawa daga Ahlul Bayt (A.S.), wannan aya tana nuni da dawowar wasu muminai Shi’ar Imam Mahdi (A.S.) da kuma wasu makiya a lokacin bayyanarsa.

Wata aya da ke nuni da raj’a

“وَحَرَامٌ عَلَىٰ قَرْيَةٍ أَهْلَكْنَاهَا أَنَّهُمْ لَا يَرْجِعُونَ.”

“Kuma an haramta wa wata alƙarya (ko al’umma) da Muka halaka, cewa ba za su dawo ba.” (Suratul Anbiya, 95)

Wannan ita ma babbar hujja ce ga raj’a, saboda a kiyama duk mutane (matattu) za su tashi — waɗanda aka halaka da waɗanda ba a halaka ba. Don haka kalmar “la yarji‘un” tana nuni ne da dawowa duniya, ba dawowa kiyama ba.

Imam Baƙir da Imam Sadiƙ (A.S.) sun ce:

«فهذه الآیة من أعظم الدلالة فی الرجعة، لان أحدا من أهل الاسلام لا ینکر أن الناس کلهم یرجعون إلی القیامة، من هلک ومن لم یهلک، فقوله: «لا یرجعون» عنی فی الرجعة، فأما إلی القیامة یرجعون حتی یدخلوا النار.»

"Wannan aya tana daga manyan hujjojin raj’a; domin babu musulmi da yake musun cewa dukkan mutane za su koma ranar kiyama — halakakku da waɗanda ba halakakku ba. Saboda haka “لا یرجعون” yana nuni da raj’a ne. Amma a kiyama su ma za su tashi har su shiga wuta.

Wannan tattaunawar zata ci gaba...

An ɗauko daga littafin “Negine Afarinesh” tare da ɗan gyara.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha